Kisan Uromi: Barau ya ziyarci iyalan waɗanda aka kashe, ya ba su kyautar N16m

Date:

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin, ya ziyarci iyalan mafarauta 16 da aka kashe a yankin Uromi da ke Jihar Edo, tare da ba su tallafin Naira miliyan 16.

Matan matatan sun fito ne daga ƙananan hukumomin Bunkure, Kibiya, Rano, da Garko a Jihar Kano.

InShot 20250309 102403344
Talla

Barau ya gana da iyalan mamatan a Masallacin At-Taqwa da ke Bunkure a ranar Laraba tare da Ministan Harkokin Gidaje, Yusuf Abdullahi Ata da sauran manyan jami’ai.

Barau, ya yi ta’aziyya da kuma tabbatar da cewa waɗanda suka aikata laifin za su fuskanci hukunci.

“Na zo nan ne domin na taya ku jaje kan wannan mummunan al’amari da ya jawo rasuwar ’yan uwanku 16 a ranar Alhamis da ta gabata.

Murtala Garo ya mika ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi

“Allah Ya Aljanna Firdausi ta zama makomarsu, Ya bai wa waɗanda suka ji rauni lafiya,” in ji Barau.

“Ba za mu ɗauki hakan da sauƙi ba. Za mu tabbatar cewa waɗanda suka aikata laifin za su fuskanci hukunci.”

Barau, ya kuma sanar da bai wa kowane daga cikin iyalan mamatan kyautar Naira miliyan ɗaya, wanda ya kai jimillar Naira miliyan 16.

Da yake magana a madadin iyalan mamatan, Sheikh Zainul Abidina Auwal, limamin yankin, ya gode wa Barau bisa ƙoƙarinsa da yadda ya damu da lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...