Gwamnan Kano ya bada guraben aikin gwamnati ga ɗaliban da ya kai ƙasar waje karatu

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ɗauki ɗalibai 54 aiki bayan sun kammala karatun digiri na biyu a kan harkar kiwon lafiya a kasar waje.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya aikowa Kadaura24.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ya ce gwamnan ya sanar da bada guraben aikin ne a liyafar buɗe-baki da ya yi da daliban, wanda su ka dawo daga India bayan sun yi karatun na shekara ɗaya a jami’ar Symbiosis International University a Ranar Juma’a.

Ya ce tuni an kammala duk wasu tsare-tsare ga ɗaliban na su fara aiki a asibitocin gwamnati domin inganta harkar lafiya a jihar.

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Ya kuma hore su da su yi amfani da ƙwarewar da su ka samo lokacin da su ke karatun a India a yayin gudanar da aiyukan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...