Kotu a Kano ta yankewa wasu ƴan TikTok ɗaurin shekara guda a gidan yari

Date:

 

 

Kotun Majistiri da ke zamanta a gini mai lamba 47 unguwar Norman’s land da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano ta aike da wasu ƴan TikTok biyu gidan yari na shekara guda amma da zaɓin tara.

RFi ta rawaito cewa kotun ta samu ƴan TikTok ɗin biyu da laifin wallafa wasu bidiyo na rashin ɗa’a waɗanda suka ci karo da addini da kuma tarbiyyar jihar ta Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Tun farko hukumar tace fina-finai ta jihar ce ta kame ƴan TikTok ɗin biyu waɗanda aka bayyana sunansu da Ahmad Isa da kuma Maryam Musa da suka fito daga unguwar Ladanai a yankin Hotoro na jihar, gabanin gurfanar da su gaban kotu.

Ta tabbata: NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Lauyan gwamnatin jihar Barista Garzali Maigari Bichi ya tuhume mutanen biyu da haɗa baki wajen aikata manyan laifuka baya ga wallafa saƙon da ya ci karo da tarbiyyar addini da kuma dokokin jihar ta Kano, laifukan da dukkaninsu suka amsa aikatawa.

20250228 181700

Mai shari’a Hadiza Muhammad Hassan da ta jagoranci zaman shari’ar ta aike da mutanen biyu gidan yari na shekara guda-guda amma da zaɓin tarar Naira dubu 100 kowannensu.

Haka zalika zaman shari’ar ya hori matasan biyu da su kasancewa masu ɗa’a da kuma bin dokokin jihar da addinin Islama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...