Kakakin Rundunar yansadan Kano ya ziyarci kwamishinan yada labarai

Date:

 

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ziyarci kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, domin samar da alakar inganta tsaro a jihar.

Lokacin da yake jawabi SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce sun ziyarci kwamishinan ne domin taya shi murnar mukamin da gwamnan Kano ya ba shi, sannan su kyautata alakar aiki tsakanin yan sanda da ma’aikatar yada labarai ta Kano.

Kiyawa ya jaddada cewa akwai bukatar rundunarsu ta hada kai da ma’aikatar don kyautata harkokin yada labarai da kuma shigo da mutanen Kano kan harkokin tsaron jihar.

InShot 20250115 195118875
Talla

Da yake nasa jawabin kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya yaba da ziyarar kuma ya nada tabbacin ziyarar zata kara inganta alakar ma’aikatar da Rundunar yan sadan, domin samar da ingantattun bayanai don kyautata tsaron jihar.

Ya ba da tabbacin ma’aikatar zata cigaba da aiki kafada da kafada da rundunar yan sandan don wayar da kan al’umma su fahimci muhimmancin taimakawa yan sanda don inganta tsaron jihar Kano.

Waiya ya ce Wannan kyakykyawar alakar zata taimaka wajen kara samar da fahimtar juna tsakanin yan sanda da jama’a da don samun sahihan labaran da za su kara tabbatar da tsaro a Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...