Babban Burina shi ne Bunkasa Rayuwar Matasan Kano – Sani Danja

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada Aniyarta na taimakawa matasa don cigaban rayuwar su ta fannoni daban-daban.

Hon. Sani Musa Danja Mai baiwa gwamna Shawara Musamman kan cigaban matasa a sha’anin wasanni ne ya bayyana haka ga manema labarai a ofishin sa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sani Danja ya ce dole sai an jure wurin wayar da kan matasa Musamman wadanda suka dauki gabarin shaye-shaye ko daba, har ayi nasarar cimma burin kawar musu da mummunan tunani.

“Za mu tabbatar sun ajiye waccen dabi’ar sannan mu samar musu da ilimi, yadda za su zama abin koyi kamar yadda jagoran kwankwasiyya yayi har aka cimma nasara a kwankwasiyya, kuma Gwamna shi ma ya gada”.

Maulidin Inyass: Kashim Shattima ya Jinjinawa Mabiya Darikar Tijjaniyya na Nigeria

Sani Danja ya ce yana da manufofin bunkasa rayuwar matasan jihar Kano, din haka ya ce zai yi iya kokarinsa don cimma wadancan manufofi.

Daga nan mai baiwa Gwamnan Shawara kan cigaban matasa da sha’anin wasanni Sani Danja ya ce, idan har muka bada gudunmawa kasa zata canja kuma ta gyaru musamman ta hanyar Taimakon Mutane don cigaban jihar kano.

Karshe ya ce matasa sune kashin bayan cigaban Al’umma, don haka wajibi a tsaya tsayin daka don inganta rayuwarsu, Domin idan matasan Kano suka gyaru za su zama masu kishin jihar, hakan zai sa su rika yin abubuwa masu amfani da kowacce jiha a kasarnan zata yi koyi da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...