Gwamnan Kano Ya Tallafawa Matasa 340 Da Suka Kammala Makarantar Kiwo da Rainon Tsirrai

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya raba shanu, raguna, da kayan aikin lambu na zamani ga matasa 340 da suka kammala karatunsu a cibiyoyin kiwon dabbobi da rainon tsirrai a Jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya aikowa Kadaura24 ranar Laraba.

Gwamnan ya sanar da cewa kowane mutum cikin wanda suka kammala karatun zai samu bijimin sa biyu ko raguna biyu, tare da abincin dabbobin na watanni uku.

InShot 20250115 195118875
Talla

Gwamnan ya ce Wannan shiri, wani bangare ne na kokarin gwamnatinsa na rage radadin talauci da kuma karfafa gwiwar matasa jihar domin su zamo masu dogaro da kawunansu.

A cewar sanarwar, Gwamna Yusuf ya jaddada cewa shirin na nuni ne da yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen inganta rayuwar matasa da samar da abinci, wadanda ke da matukar muhimmanci wajen tabbatar da ci gaban jihar Kano.

Yadda Gwamnatin Kano ta yi Rinton Aiki a Dawakin Tofa – Bincike

Wadannan matasa 340 su ne rukunin farko na dalibai da aka yaye a cibiyar kiwon dabbobi da rainon tsirrai da ke Bagauda a karamar hukumar Bebeji, biyo bayan bude cibiyar da gwamnati mai ci ta yi.

Gwamnan ya kara da cewa, an sake yi wa wasu matasa 340 rajista a karo na biyu.

“Daliban da aka yaye a wannan cibiya yanzu za su iya dogara da kawunan don inganta rayuwarsu da taimakawa wasu.

Gwamnan ya ja hankalin wadanda suka amfanan da su hada kai ta hanyar kafa kungiyoyin domin su rika tattauna yadda za su ciyar da sana’arsu gaba.

Ya kuma baiwa dukkanin wadanda suka kammala karatun aikin rainon tsirrai kayan aiki na zamani tare da jari na Naira 100,000 don tallafa musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...