Jami’ar Dutsin-ma ta zata samar da reshenta a birnin Kano – Shugaban Jami’ar

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi.

 

Jami’ar tarayya dake Dutsen-ma a jihar Katsina tasha alwashin bude cibiyar Karatu a cikin birnin Kano domin ba da dama ga matasan dake aiki su sami damar cigaba da karatu ba tare da samun wani tsaiko ba.

Shugaban jami’ar Farfesa Armaya’u Hamisu Bichi ne ya bayyana hakan yayin taron tattaunawa da Kungiyar ‘yan jarida ‘yan Asalin karamar hukumar Bichi a rana a Asabar.

Talla

Farfesa Armaya’u ya ce bisa gano cewar nisa da kuma yanayin aiki dake hana wasu musamman masu sha’awar yin karatu a Jami’ar, a yanxu yana shirye shiryen bude cibiyar karatu ta Jama’ar a cikin garin Kano don saukakawa ma’aikata da ‘yan kasuwa.

Inganta Ilimi: Gwamnan Kano zai raba kayan makaranta ga dalibai sama da 789,000

Ya kuma yaba da ziyarar da ‘yan jarida ‘yan Asalin Bichi suka kai masa, inda ya ce hakan zai kara kulla alakar aiki tsakaninsa dasu musamman a bangaren abinda ya shafi cigaba karamar hukumar ta Bichi.

Ya kuma bayyana cewar har yanxu kafafen yada labarai na Radio da Talabijin da Jaridu su ne sahihan hanyoyin samun ingantaccen labarai, sai dai ya ce akwai bukatar yin duba akan yadda ake amfani da kafafen sada zumunta wajen yada labaran karya da cin zarafin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...