Yanzu-yanzu: Guda cikin kwamishinonin da gwamnan Kano ya sauke ya koma APC

Date:

Tsohon kwamishinan ma’aikatar raya karkara ta jihar Kano Alhaji Abbas Sani Abbas ya sauya sheka daga NNPP Kwankwasiyya zuwa Jam’iyyar APC.

” Na bar waccan tafiyar ne saboda abubuwan da ake na rashin adalci ga wadanda muka taho da su”.

Alhaji Abbas Sani Abbas ya bayyana hakan ne jim kadan bayan da mataimakin shugaban majalisar dattawa Sanata Barau Jibrin da Abdullahi Abbas suka cire masa har hularsa.

Talla

Tsohon kwamishinan ya ce gwamnatin Kano ta gaza taimakawa mutanen da suka sha wahalar kafa ta , ta hanyar amfani da karfinsu da dukiyoyinsu da basirarsu, amma an sami dama an gaza taimaka musu.

” APC dama gida ce a waje na domin da mu aka kafa ta , don haka daga yau na bar Jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya na dawo Jam’iyyar APC”.

Kotun Daukaka Kara ta Bayar da Umarnin Sake Sauraron Shari’ar Masarautar Kano

Ya kuma sha alwashin ba da duk wata gudunmawa da ake bukata domin samun nasarar Jam’iyyar a zabuka masu zuwa.

A nasa jawabin Sanata Barau Jibrin ya yabawa tsohon kwamishinan bisa dawowar da yayi gidansa, inda ya ce dama kaddarace ta sa ya bar ta yanzu kuma ga shi ya dawo.

Ya yi masa Maraba, sannan ya ba da tabbacin jam’iyyar APC za ta cigaba da yin duk mai yiwuwa domin ganin duk dan APC dake Kwankwasiyya ya dawo gidansa na asali.

Kadaura24 ta rawaito Abbas Sani Abbas dai yana cikin kwamishinonin 5 da gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sauke a kwanakin baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...