Ana barazana ga rayuwata – Peter Obi

Date:

Ɗantakarar shugaban ƙasa a Jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce ana yi wa rayuwarsa barazana saboda sukar gwmnatin Shugaban Ƙasa Tinubu da ya yi a saƙonsa na sabuwar shekara.

A saƙon nasa na sabuwar shekarar, Obi ya bayyana cewa Najeriya na fama da taɓarɓarewar tattalin arziki da rashin tsaro da rashin ingantaccen kiwon lafiya.

Talla

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce, “shin na wuce iyaka? na yi wannan tambayar ce saboda ana yi wa rayuwata da ta iyalina barazana saboda jawabin da na yi na sabuwar shekara. Bayan barazanar kuma, wani mai suna Mr Felix Morka ya zarge ni da wuce iyaka, sannan ya yi barazanar zan ɗanɗana kuɗata,” in ji shi.

Obi ya ƙara da cewa idan har da gaske ya karya doka, a nuna masa, inda ya ƙara da cewa, “amma ba zan daina faɗin gaskiya ba, musamman a wannan lokacin da ƙasarmu ke ƙara shida cikin ruɗu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...