Da Dumi-Dumi: NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kamfanin man NNPCL a Nijeriya ya zaftare farashin litar fetur zuwa N899 irin na Dangote.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar PETROAN Joseph Obele ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema a ranar asabar.

Sanarwar ta ce sashin Kasuwanci na NNPC ta fitar da sabon farashin man kamar haka: Lagos, N899.0; Warri, N970.0; Oghara, N970.0; Port Harcourt, N970.0. sai kuma Calabar, N970.0.

Talla

Kamfanin NNPLC ya yi wannan ragi ne bayan da matatar mai ta Ɗangote ta fitar da sanarwar rage farashin man.

Da yake tsokaci kan rage farashin man Shugaban kungiyar PETROAN Billy Gillis Hary ya ce rage farashin man zai samar da sauki ga masu ababen hawa musamman a wannan lokaci na bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara.

Fulawa Da Dabbobin Fadar Shugaban Ƙasa Za Su Ci N125m A 2025

” Muna yaba wa Kamfanin NNPLC bisa rage yawan kudin litar mai, wanda hakan ya nuna kwazon kamfanin na samar da sauki ga yan Nigeria”.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a ranar 19 ga watan Disamba, 2024, kamfanin NNPLC ya rage farashin man kafin wannan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...