Kotu Ta Yanke Wa Wani Matashi Hukuncin Rataya A Kano

Date:

Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin kisa ta hanyar rataya a Jihar Kano kan laifin aikata kisa a wurin bikin Ι—aurin aure.

Babbar Kotun Jihar Kano ta kuma yanke wa matashin mai suna Abba Suleiman hukuncin Ι—aurin shekara biyar a gidan yari kan laifin hada baki da aikata laifi.

Talla

Mai Shari’a Amina Adamu ta yanke wa Abba hukuncin ne tare da wasu abokansa da suka tsere, bayan samun su da laifin caka wa wan mai suna Iliyasu Tasi’u wuka har lahira a yayin bikin auren.

Kasafin 2025: Engr. Sani Bala Tsanyawa ya gabatar da wasu muhimman batutuwa guda biyu a majalisa

An fara gurfanar da Abba a kotun ne 2019 bayan an kama shi yana Ζ™oΖ™arin hana kai wata amarya dakin mijinta a unguwar Sauna Kawai da ke Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jihar.

A lokacin taΖ™addamar ce wanda a ake zargin ya aikata kisan da aka yanke masa hukumci a kai.

Bayan sauraron lauyoyi da shaidun masu kara da wanda ake Ζ™ara, AlΖ™ali Amina Adamu ta ce masu kara sun gabatar da gamsassun dalilai da ke tabbatar da laifin wanda aka gurfanar don haka ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya da kuma Ι—aurin shekara biyar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related