Wani mai aikin sharar asibiti a Kano ya mayar da kudin da ya tsinta kimanin Naira miliya 40 ga mai su.
Malam Aminu Umar Kokar Mazugal ya tsinci kudin ne a dalolin Amurka a cikin wata jaka da mai su ya manta a Asibitin Abubakar Imam da ke unguwar Fagge.

Malam Aminu wanda matsakaicin maβaikaci ne ya tsinci kudin a cikin wata jaka kuma ya mayar da kudin ga mai su, Alhaji Ahmed Abubakar, wanda ya manta da su a lokacin da ya je dubiyar mara lafiya a asibitin.
Alhaji Ahmed ya manta da kudin ne a wurin da ya dan zauna na dan lokaci a wurin ajiye motoci da ke kusa da masallaci, inda daga bisani ya wuce domin shiga jirgin sama.
Gwamnatin Kano ba zata saurarawa masu sayar da filaye ba bisa ka’ida ba – Kwamitin karta kwana
Malam Aminu ya shaida wa wakilin Daily trust cewa jim kadan da tafiyarsa mutumin ne shi kuma ya tsinci kudin a lokacin da yake aikin shara.
Ya ce daga bisani, bayan kimanin awa guda, mai kudin ya dawo yana cigiya, shi kuma ya mayar masa da kayansa.
Ya ce mai kudin ya yi masa kyauta amma ya ki amsa, duk da cewa ya ba shi lambar wayarsa, kuma mutumin ya yi alkawarin tuntubar sa idan ya dawo daga kasar waje.
Shugaban Asibitin, Dokta Aminu Imam Yola, ya tabbatar da faruwar lamarin yana mai cewa hukumar gudanarwar asibitin ta sanar da Maβaikatar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano domin a karrama Malam Aminu.