Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya dauki matakin magance matsalolin da daliban Kano wadanda gwamnatin Ganduje ta tura karatu kuma suka kasa karbar shaidar kammala karatunsu.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24 a ranar Litinin, ta bayyana cewa gwamna Yusuf ya yi wata muhimmiyar ganawa da mahukuntan jami’ar Near East da ke Cyprus domin shawo kan lamarin.
Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan batun bayar da satifiket ga daliban Kano da suka kammala karatunsu a shekarar 2015 zuwa 2019.

Da yawa daga cikin wadannan daliban da aka yaye, musamman wadanda suka yi karatu a fannonin aikin likitanci da aikin jinya, sun kasa samun damar yin aikin da suka koya, sakamakon gaza biyan kudin makaranta da gwamnatin Ganduje ta yi.
Gwamnatin Kano ta yi Martani Kan Hana Sarki Sanusi Kai Hakimin Bichi
Gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban koma-baya, ba wai ga daliban da abin ya shafa ba, har ma da jihar, wadda take da bukatar kwararru jami’an kula da lafiya.
Gwamnana Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa zata biya duk kudaden da ake bin daliban domin su karɓi Satifiket dinsu don su fara amfani da abun da suka koya domin amfanin al’umma.