Da dumi-dumi: Jami’an tsaro sun kewaye gidan Sarkin Kano Sanusi tare da hana shige da fice

Date:

 

A yau safiyar Juma’a an tashi da ganin jami’an ƴansanda ɗauke da makamai tare da na DSS sun yi ƙawanya a Masarautar Kano, inda Sarki Muhammadu Sanusi ll ke zaune.

Rahotanni da jaridar kadaura24 ta samu sun nuna cewa jami’an tsaron sun hana shige da fice a gidan Sarkin.

Talla

Rahotanni sun baiyana cewa a yau din ake sa ran Sarki Sanusi zai raka sabon Wamban Kano, Munir Sanusi zuwa Bichi, inda zai yi hamkimci.

Haka a binciken da Jaridar Kadaura24 ta gudanar ta gano can ma fadar Bichi dake garin Bichi an zuba jami’an tsaro, mai yiwuwa da nufin hana zuwan sabon Wamban Kano da Sarki Sanusi II na nada .

Gwamnatin Kano ta Haɗa Kai da Ofishin Jakadancin Nijeriya a Indiya Don Inganta Walwalar Daliban Kano

An dai zara a yau sarki Sanusi II zai kai wanban na Kano a marsayin hakimin Bichi, ya kuma gudanar da zaman fadanci daga bisani ya jagoranci sallar juma’a a Babban masallacin masarautar ta Bichi.

Ga hotunan yadda gidan Sarki na Kofar kudu yake a wannan safiyar.

Ga kuma hotunan yadda gidan Sarkin Bichi yake a wannan safiyar

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...