Ku rika bincike da neman ilimi don inganta aiyukanku – Amb. Waiya ga yan jarida

Date:

Daga Abubakar Yakubu

 

Shugaban kungiyar nan mai zaman kanta ta Citizen for Development and Education ( CDE) Amb. Ibrahim Waiya ya bukaci yan jarida da su kasance masu yawaita bincike da neman ilimin domin kyautata Aikinsu da samun damammaki.

” Akwai damammaki da yawa da ake samu a kasashen duniya, kuma ba zaka same su ba sai ka fadada kunaninka ka zamo mai kirkira ta fannin aikinka, hakan shi zai sa kafafen yada labarai na kasashen wajen su nemeka kar ka cimma burkina na rayuwa”.

Amb. Ibrahim Waiya ya bayyana hakan ne yayin wata bitar yini guda da kungiyar ta CDE ta shiryawa yan jarida a kano kan yadda za su inganta aiyukansu.

Talla
Talla

Ya ce aikin jarida a wannan lokacin yana samun sauye-sauye musamman saboda zuwan sabbin fasahohi , don haka akwai bukatar yan jarida a rika karbar sauye-sauyen domin aiyukansa su rika tafiya dai-dai da zamani.

Ban ce na goyi bayan Ƙudirin gyaran dokar Haraji dari bisa dari ba, Ina bada Hakurin Rashin Fahimta ta – Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa

” Mun shirya muku wannan bitar ne domin sake tunatar da ku muhimmancin bin ka’idoji da dokokin aikinku , don al’umma su amfane ku yadda ya kamata saboda kuna da matukar muhimmaci a cikin al’umma shi yasa muke so ku inganta aiyukan naku”. Inji Amb. Waiya

Amb. Ibrahim Waiya ya sha alwashin cigaba da hada kai da yan jarida domin samar da cigaba mai ma’ana ga al’ummar jihar Kano da kasa baki daya.

Dr. Bala Muhammad na Jami’ar Bayero dake Kano ya gabatar da makala mai taken “Bin ka’idoji da dokokin aikin jarida ga Manema labarai, yayin da shi kuma Dr. Nuhu Musa Idris shi ma daga jami’ar Bayero ya gabatar da makala mai taken ” Rabe-raben Gwamnatin Nigeria da dokokinsu”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...