Daga: Aliyu Danbala Gwarzo
Alhaji Sani yanmedi Shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Gezawa, ya ba da tallafin atamfofi ga da daliban da suka sauke al’qur’ani mai girma a makarantar Tarbiyyatul Aulad dake jannarya a karamar hukumar Gezawa.
Alhaji Sani yanmedi ya ce ya ba da kyautar Atamfofin tare da kudin dinki naira Dubu Dari domin kara zaburar da daliban wajen cigaba da kokarin zuwa makaranta domin samun ilimin Addini, ya ce kuma hakan zai sa sauran dalibai na baya su kara zage dantse wajen cigaba da zuwa makaranta.

Ya kara da cewa “Hakika irin wadannan Dalibai ya dace a rika kokarin taimaka musu duba da yadda suka maida hankali wajen zuwa makaranta har Allah ya ba su damar sauke Al’qur’ani mai girma, dan haka babu tukuicin da ya kamata a yi wa daliban sai da irin wanan tagomashi kuma ashirye muke mu cigaba da tallafawa makaratun islamiyyu da dalibai a Gezawa baki daya.
Sanya Al’adu A Fina-Finai Na Iya Inganta Harkar A Nahiyar Afirika – KILAF
Kazalika Shugaban jam’iyyar ya yi kira ga matasa da su maida hankali wajen neman ilimin Addini domin shi ne zai taimake su a duniya da lahira.
Daga karshe ya yi wa wadannan dalibai fatan Alkairi tare da Fatan za su yi amfani da abin da suka karanta domin samarwa da kansu gobe mai kyau.