Ƙanin Kwankwaso ya maka Gwamna Abba Gida-Gida a Kotu akan Batun Fili

Date:

 

Garba Musa Kwankwaso, ƙanin tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shigar da kara a gaban kotu domin ta hana gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar daukar wani mataki a kan wani fili.

A cikin karar har da hukumar KNUPDA da Kwamishinan Shari’a na jiha da sauran wasu mutane.

DAILY NIGERIAN ta jiyo cewa asalin filin Kwankwaso ne ya baiwa wani kamfani mai suna WAECO, amma sai gwamna Abdullahi Ganduje ya kwace filin.

Talla

Daga baya sai hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta tabbatar da kwace filin, wanda ya ke a rukunin gidaje na Kwankwasiyya City, bisa hujjar cewa lokacin da su ka bada filin ga Kamfanin WAECO bai yi rijistar zama cikakken kamfani ba.

Daga nan ne sai Ganduje ya dawo da kasuwar yan magani cikin wani bangare na filin.

Zaɓen Kananan hukumomi: Gwamnatin Kano ta nemi a sauya alƙalin da zai yi Shari’ar

Shi ma Abba da ya hau, sai ya ƙi maidawa kamfanin WAECO filin, shi ne Garba Kwankwaso ya shigar da kara.

A umarnin da ya bayar, Mai Shari’a Usman Na’abba ya bada umarnin hana taba filin ga gwamnati, sannan ya dage sauraren koken zuwa 27 ga watan Nuwamba.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...