Kwamitin amintattun KCSF ba shi da hurumin dakatar da ni – Ibrahim Waiya

Date:

Shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula da ke jihar kano Amb. Ibrahim Waiya ya ce har yanzu shi ne halastaccen shugaban gamayyar kungiyoyi masu zaman kansu na jihar Kano.

“Wannan sanarwar data fita mai ɗauke da sa hannun sakataren kwamitin amintattu su sani cewa a dokance basu da hurumi na tsige mamba a ƙungiya balle shugaba.

Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga Amb. Waiya kan harkokin yada labarai Bashir A Bashir ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Ya kara da cewa “Muna tabbatar da cewa masu shirin tada wannan tarzoma ba don komai suke ba, sai don wani kuɗiri na ƙashin kansu, wanda ba cigaba ne ga al’ummar jihar Kano ba.

Zanga-zangar yunwa: Gwamnan Kano ya baiwa mutane biyu aiki cikin matasa 76 da aka mikasu ga iyayensu

“A saboda haka muna kira ga mambobin gamayyar kungiyoyi masu zaman kansu na jihar Kano da suyi fatali da wannan sanarwar tare da jiran me kotu zata faɗa a mako mai zuwa”. Inji sanarwa

Sanarwar ta ce Ibrahim Waiya yana ƙara haƙurƙuntar da mambobin KCSF musamman masu kishin jihar Kano na tabbatar da samun Nasara a gaban kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...