Da dumi-dumi: Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya ciyo bashin $2.2bn

Date:

Majalisar dattawa ta amince da bukatar shugaban kasa Bola Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.2.

Majalisar dattijai ta amince da bukatar ciyo bashin ne bayan da ta yi nazari kan rahoton Aliyu Wamakko, shugaban kwamitin kula da basussukan cikin gida da na kasashen waje.

Talla

Kudaden da Tinubu zai ciyo bashin a kudin Naira ya kai kwatankwacin Naira Tiriliyan 1.7 , za dai a yi amfani da Kudaden ne domin cike gibin Naira Tiriliyan 9.1 a kasafin kudin 2024.

kamfanoni kusan 300 ne ake sa rai za su halarci baje-kolin kasuwar duniya ta Kano – KACCIMA

A ranar talata ne dai Shugaba Tinubu ya bukaci majalisar dattawan da ta amince masa ya ciyo wannan bashin.

Majalisar zartaswa ta Nigeriya (FEC) ce ta fara amincewa a da shirin karɓo bashin na dala biliyan 2.2 don “karfafa kudaden kasar da kuma bunkasa tattalin arzikin kasar”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...