Lugudan Wuta da sojojin Nigeria ke yi ya tilastawa Lakurawa tserewa daga jihohin Kebbi da Sakkwato

Date:

 

 

Mambobin kungiyar ƴan ta’adda ta Lakurawa sun fara tserewa yayin da sojoji suka kara kaimi wajen kai hare-haren kasa da na sama a sansanonin kungiyar a fadin jihohin Kebbi da Sokoto.

Talla

Daily Trust ta rawaito cewa biyo bayan harin da kungiyar Lakurawa ta kai a garin Mera a karamar hukumar Augie ta jihar Kebbi, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 17, shelkwatar rundunar soji ta tura wasu dakarun sojoji zuwa yankin.

Gwamantin Kano za ta fara Kama Yaran da suke yawo a titunan birnin

A lokacin da suka isa Birnin Kebbi, dakarun, kamar yadda Abdullahi Idris Zuru, mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai na gwamnan Kebbi ya bayyana, sun gana da mataimakin gwamna Abubakar Umar Tafida a Ofishin Majalisar Zartarwa kafin su wuce zuwa Mera.

Zuru ya ce dakarun sun samu nasarar korar ‘yan bindigan tare da kwato shanun sata da suka bari a lokacin da ‘yan ta’addan suka tsere.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...