Dalilin da Yasa Gwamantin Kano ta Maka Mawaki Rarara a Gaban kotu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano karkashin jagorancin Abba El-mustapha ta gurfanar da mawaki Dauda Kahutu Rarara a gaban Kotu bisa zargin da sakin wata sabuwar waka batare da salewar Hukumar ba.

A wata sanarwa da jami’in yada labarai na na Hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya aikowa kadaura24, ya ce tun kafin wannan lokaci Hukumar tace fina-finai ta aikawa da mawakin sakon korafi dangane da sabuwar wakar daya saki ba tare da ya kawo an tace ba sai dai mawakin bai bata amsa dangane da korafin da ta aika masa ba wanda hakan ne dalilin da ya sa Hukumar ta garzaya gaban kotun domin kowa zaman doka yake a cewa jami’in Hulda da jama’a na Hukumar.

Wakilan Hukumar a kotu ya tabbatar da cewa tuni kotun ta aikawa da mawakin takardar gayya ta sammaci sai dai ba’a ga fuskar mawakin a kotu ba a yau 13 ga watan nuwamba a yayin zamanta.

Talla

Tun kafin wannan lokacin bayan sakin sabuwar wakar Hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jahar Kano ta turawa mawakin sakon neman ba’asi ta hanyar sakon karta kwana sai dai har kawo ya wannan lokaci mawakin bai maidawa da Hukumar amsar sakon ba.

Rikicin NNPP: Dungurawa ya yiwa Sanata Kawu Sumaila Martani

Duk da cewa jami’in hulda da jama’a na hukumar tace Fina-Finan bai bayyana kowacce waƙa ba ce, amma binciken da Jaridar Kadaura24 ta gudanar ya gano cewa an gurfanar da mawakin ne saboda sakin waƙar ” Abba tsaya da kafarka”.

 

Kamar yadda kowa ya sani ne tace fina-finai, rubuce-rubuce tare da waka na daya daga cikin manyan aiyukan da suka rataya akan Hukumar domin tabbatar da tsafta tare da dora komai a bisa doron doka da oda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...