Kotu ta hana CBN riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano

Date:

Daga Sani Sani Idris

 

Babbar Kotun Jihar ta hana Babban Bankin Nijeriya (CBN) da Gwmanatin Tarayya riƙe kuɗaɗen ƙananan hukumomin jihar 44 na wata-wata.

Kotun ta bayar da umarnin wucin gadin ne ga Gwamantin Tarayya da hukumominda ma’aikatunta, bayan ƙarar da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Nijeriya (NULGE) da wasu masu kishin Jihar Kano.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Ibrahim Musa Muhammad, ya ba da umarnin ne ga CBN da Hukumar Rabon Kudaden Shiga na Kasa da Kuma Akanta-Janar na Tarayya kan tabawa, rikewa ko jinkirin sakin kudaden kananan hukumomin na jihar Kano.

Talla

Ya ba da umarnin ne kan karar da masu karar suka nuna damuwa cewa game da yiwuwar rikewa ko jinkirin kudaden kananan hukumomin ko wani bangaren kudaden.

Cire Kwamishiniyar jin ba zai Haifawa gwamnatin Kano da mai Ido ba – Shugaban APC Integrity

Alkalin ya kuma umarci hukukumomin gwamantin da wakilansu da kada su kuskura su yi duk wani nau’in katsalandan kan kudaden kananan hukumomin.

Daga nan ya dage zaman zuw ranar 21 ga watan nan na Nuwamba, 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...