Kotu ta hana CBN riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano

Date:

Daga Sani Sani Idris

 

Babbar Kotun Jihar ta hana Babban Bankin Nijeriya (CBN) da Gwmanatin Tarayya riƙe kuɗaɗen ƙananan hukumomin jihar 44 na wata-wata.

Kotun ta bayar da umarnin wucin gadin ne ga Gwamantin Tarayya da hukumominda ma’aikatunta, bayan ƙarar da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Nijeriya (NULGE) da wasu masu kishin Jihar Kano.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Ibrahim Musa Muhammad, ya ba da umarnin ne ga CBN da Hukumar Rabon Kudaden Shiga na Kasa da Kuma Akanta-Janar na Tarayya kan tabawa, rikewa ko jinkirin sakin kudaden kananan hukumomin na jihar Kano.

Talla

Ya ba da umarnin ne kan karar da masu karar suka nuna damuwa cewa game da yiwuwar rikewa ko jinkirin kudaden kananan hukumomin ko wani bangaren kudaden.

Cire Kwamishiniyar jin ba zai Haifawa gwamnatin Kano da mai Ido ba – Shugaban APC Integrity

Alkalin ya kuma umarci hukukumomin gwamantin da wakilansu da kada su kuskura su yi duk wani nau’in katsalandan kan kudaden kananan hukumomin.

Daga nan ya dage zaman zuw ranar 21 ga watan nan na Nuwamba, 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...