Dan majalisar tarayya na NNPP daga Kano ya fice daga Kwankwasiyya

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Dan majalisar tarayya mai wakilar karamar hukumar Dala a jihar kano, Aliyu Sani Madakin Gini ya bayyana ficewarsa daga tafiyar Kwankwasiyya dake biyayya da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Idan za a iya tunawa Aliyu Sani Madakin Gini na daga cikin na gaba-gaba a tafiyar Kwankwasiyya da yiwa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso biyayya.

Madakin Gini ya bayyana ficewarsa tasa ne daga tafiyar Kwankwasiyya da yammacin wannan rana ta lahadi a mazabar ta Dala dake jihar kano.

Talla

“Daga yau Ni Aliyu Sani Madaki na bar tafiyar Kwankwasiyya, Saboda Kwankwasiyya yaudara ce, Kwankwasiyya cin amana ce, Mai girma Gwamnan jihar Kano Alh. Abba Kabir Yusif mutumin kirki ne, ina baka shawara ka tsaya da kafarka ka da aje fa ka wani rami da bazan bayyana shi yanzu ba”. Inji Ali Madaki.

Ya ce ya shirya tsaf domin tallafawa duk wanda ya biyo shi, yace kowa zai amfana, ya yi alkawarin zai share sama da Kwana 7 domin ganawa da magoya bayansa.

Ku hanzar ta fara aiki a harabar MAAUN dake Gwarzo don inganta Ilimi – T Gwarzo ga Farfesa Adamu Gwarzo

Ya umarci duk wani wanda ya yarda cewa shi ne Jagoransa, ya cire jar hula da jajayen mayafai.

Sai dai dan majalisar bai bayyana ficewarsa daga jam’iyyar NNPP ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...