Dan majalisar tarayya na NNPP daga Kano ya fice daga Kwankwasiyya

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Dan majalisar tarayya mai wakilar karamar hukumar Dala a jihar kano, Aliyu Sani Madakin Gini ya bayyana ficewarsa daga tafiyar Kwankwasiyya dake biyayya da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Idan za a iya tunawa Aliyu Sani Madakin Gini na daga cikin na gaba-gaba a tafiyar Kwankwasiyya da yiwa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso biyayya.

Madakin Gini ya bayyana ficewarsa tasa ne daga tafiyar Kwankwasiyya da yammacin wannan rana ta lahadi a mazabar ta Dala dake jihar kano.

Talla

“Daga yau Ni Aliyu Sani Madaki na bar tafiyar Kwankwasiyya, Saboda Kwankwasiyya yaudara ce, Kwankwasiyya cin amana ce, Mai girma Gwamnan jihar Kano Alh. Abba Kabir Yusif mutumin kirki ne, ina baka shawara ka tsaya da kafarka ka da aje fa ka wani rami da bazan bayyana shi yanzu ba”. Inji Ali Madaki.

Ya ce ya shirya tsaf domin tallafawa duk wanda ya biyo shi, yace kowa zai amfana, ya yi alkawarin zai share sama da Kwana 7 domin ganawa da magoya bayansa.

Ku hanzar ta fara aiki a harabar MAAUN dake Gwarzo don inganta Ilimi – T Gwarzo ga Farfesa Adamu Gwarzo

Ya umarci duk wani wanda ya yarda cewa shi ne Jagoransa, ya cire jar hula da jajayen mayafai.

Sai dai dan majalisar bai bayyana ficewarsa daga jam’iyyar NNPP ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...