Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Tsohon karamin Ministan gidaje da raya burane Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ya sha alwashin baiwa sabon ministan da ya gaje shi Yusuf Abdullahi Ata duk wata gudunnawa da ta dace domin ya sami nasarar sauke nauyin da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya dora masa.
“Ina baka tabbacin zan baka duk wata gudunnawa da kake bukata daga gare ni domin cigaban ma’aikatar da Nigeria baki daya”.

Abdullahi Tijjani Gwarzo ya bayyana hakan ne cikin wani sako da ya wallafa a sahihin shafinsa na Facebook na taya Ata murnar tantance shi da majalisar dattawa ta yi a jiya laraba domin kasamcewa ministan Gidaje kuma dan majalisar zartarwa ta kasa.
” Ina baka shawarar ka hada kai da Babban ministan wannan ma’aikata wato Arc. Ahmad Musa Dangiwa domin ku yi aiki tare domin tabbatar da kudirin shugaban kasa Bola Tinubu na inganta harkokin gidaje da raya burane a Nigeriya”.
Ma’aikatan shara a kano sun zargi Danzago da hana su Albashinsu na watanni 6
T Gwarzo ya kuma ta ya Yusuf Abdullahi Ata murna da majalisar dattawa ta tantance shi kuma ta amince da nadin da Shugaba Tinubu ya yi masa a matsayin ministansa.
Ya yi fatan sabon ministan zai yi aiki cikin kwanciyar hankali kuma ya gama lafiya ba tare da wata matsala ba.