Rikicin PDP: Ibrahim Little da Wali sun zargi Shekarau da kassara Jam’iyyar a Kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Wani tsagi na jam’iyyar PDP reshen jihar Kano karkashin jagorancin Ibrahim Al’Amin Little da Sadiq Aminu Wali sun sha alwashin dawo da martabar jam’iyyar a jihar.

Ibrahim Little ya bayyana haka ne yayin wani taron manema labarai da tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP dake fadin kananan hukumomi 44 na Kano.

Wannan mataki na daya daga cikin kokarin da tsagin ke yi na kara tabbatar da tasirinta da kuma dacewarsa a harkokin siyasar jihar.

Talla

Ya ce yunkurin da tsagin ke yi na farfado da martabar jam’iyyar PDP a Kano na da matukar muhimmanci, duba da irin gwagwarmayar da jam’iyyar ta yi a jihar Kano.

Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta Kasa

An zargi PDP a karkashin bangaren Malam Ibrahim Shekarau da haifar da rikice-rikicen da ba su dace ba wanda yace hakan ya jawo rabewar Jam’iyyar zuwa gida biyu.

Abubunwan da aka cimma a taron gwamnoni da Sarakunan Arewacin Nigeria

“Wannan taron da mukai wani bangare ne na matakan da muka fara dauka domin farfado da martabar jam’iyyar PDP a jihar”. Inji Little

Ya kara da cewa domin jaddada kudirinsu na tabbatar da akidu da kimar PDP, bangaren Little da Wali na da burin farfado da jam’iyyar a Kano da kuma kokarin ganin ta sami nasara a zabuka masu zuwa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...