Gwamnatin tarayya ta sanar da ranar dawo da wutar lantarki Arewacin Nigeria

Date:

Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce za a maido da wutar lantarki a jihohin Arewa 17 da suke fama da matsalar barna a layin Shiroro zuwa Kaduna nan da kwanaki biyar.

Mista Adelabu ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa bayan wata ganawa da yayi da shugaban kasa Bola Tinubu ranar litinin a Abuja.

Talla

Ya ce matsalar wutar lantarki da ake samu a yankin Arewacin kasar nan ya biyo bayan lalata layin Shiroro zuwa Kaduna da aka yi, babban layin da ke samar da wutar lantarki ga Arewa.

Sai dai ya ce za a gyara layin wutar a cikin kwanaki uku zuwa biyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...