Gwamnatin Najeriya za ta hukunta jihohin da suka ƙi zaɓen ƙananan hukumomi

Date:

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta ɗauki mataki a kan jihohin da suka ƙi gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi da zai tabbatar da cin gashin kai na ƙananan hukumomin kamar yadda kotun ƙolin ta zartar.

Babban lauyin gwamnatin tarayyar Mista Lateef Fagbemi, wanda ya bayyana hakan a jihar Ekiti a jiya Talata, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito ya ce ba gudu ba ja da baya a kan shirin aiwatar da hukuncin kotun ƙolin kan cin gashin ƙananan hukumomin.

Talla

Mista Fagbemi ya ce gwamnatin za ta yi nazarin dokokin jihohi a kan zaɓen ƙananan hukumomi tare da duba dalilin da ya sa wasu jihohinke jinkirin gudanar da zaɓen.

Bayanai sun nuna cewa a yanzu sama da ƙananan hukumomi 164 ne a jihohi takwas ba su yi zaben ba.

Cikakken bayani kan hukuncin da Kotu ta yi game da zaɓen kananan hukumomin Kano

Jaridar ta kuma ruwaito cewa, wasu rahotanni na nuna cewa wataƙila Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da hukuncin kotun ƙolin a kan cin gashin kai na ƙananan hukumomi nan da ƙarshen watan nan na Oktoba.

Talla

Hakan na nufin gwamnatin tarayyar za ta iya riƙe kason kuɗin ƙananan hukumomin da ba a yi zaɓe ba, kamar yadda hukuncin kotun ya ayyana.

Ƙananan hukumomin da ba a yi zaɓe ba na jihohin Katsina da Zamfara da NasarawaOndo, da Osun da Ogun da Cross Rivers.

Hukuncin kotun ya nuna cewa, saɓa doka ne gwamnonin jihohi su ci gaba da karɓa ko riƙe kason kuɗaɗen ƙananan hukumomi a ƙarƙashin asusun haɗin gwiwa na jida da ƙananan hukumomi.

Talla

Wasu gwamnonin jihohin ƙasar dai na ganin wallen hukuncin kotun.

A makon da ya wuce gwamnan jihar Anambra Farfesa Chukuma Soludo, a lokacin sanya hannu kan dokar mulkin ƙananan hukumomi ya yi gargaɗin cewa ba wa ƙananan hukumomin ƙasar 774 cikakken ƴancin cin gashin kai ka iya haifar da abin da ya kira ”gagarumar matsala” ta yarda za a kasa samar da cigaba mai ɗorewa.

BBC Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...