Ka gaggauta gabatar mana da kasafin kudin 2025 – Majalisar Nigeria ga Tinubu

Date:

Majalisar wakilai ta ja hankalin shugaban Najeriya Bola Tinubu kan yiyuwar karya tanadin dokar kashe kuɗin ƙasa idan har ya yi jinkirin gabatar da kasafin kuɗn 2025 ga majalisa.

Wannan na zuwa ne yayin da ya rage watanni biyu wa’adin kasafin 2024 ya ƙare.

Talla

Ɗan majalisar da ya gabatar da ƙudirin, Clement Jimbo, ya ja hankali cewa ya kamata a ce kawo yanzu an gabatar da kasafin kuɗin 2025 kasancewar watanni biyu kacal suka rage kafin wa’adin kasafin kuɗin bana ya ƙare.

Mun Dakatar da Fafutikar Neman Tsige Ganduje daga shugabancin APC – Matasan Arewa ta tsakiya

Majalisar wakilan ta bayyana damuwa a kan ƙurewar lokacin da ya kamata a samu domin nazari kan kasafin na baɗi kafin amincewa da shi a majalisar dokokin tarayya.

Majalisar ta yi nuni da cewa doka ta buƙaci a gabatar wa majalisa ƙiyasin kasafin kuɗi aƙalla watanni huɗu kafin shiga sabuwar shekara domin samun damar tantancewa shi da kuma amincewa.

Talla

A yanzu dai majalisar ta miƙa wannan batu ga kwamitinta a kan tsare-tsaren ƙasa.

A ranar biyu ga watan Oktoba shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa Birtaniya domin yin hutun makonni biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...