An baiwa Ganduje wa’adin Kwanaki 7 ya sauka daga mukamin shugaban APC na ƙasa

Date:

 

 

Kungiyar gamayyar kungiyoyin jami’iyyar APC na yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya sun baiwa shugaban jami’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje wa’adin kwanaki 7 da ya yi murabus daga mukaminsa cikin ruwan sanyi.

Talla

Shugaban kungiyar Hon Saleh Abdullahi Zazzaga a taron manema labarai a Jos babban birnin jihar Plateau, ya ce idan wa’adin ya kare Ganduje bai sauka ba, akwai yiwuwar ya dauki matakin shari’a a kansa.

Wannan wa’adi dai zai kare ne a ranar Litinin 14 ga watan Oktoba, 2024.

Cigaban ilimi: An bude makarantu uku da Rarara ya gina

Saleh Zazzaga dai na kalubalantar cewa a babban taron jami’iyyar da ya gudana a ranar 26 ga watan Maris, 2022, an ba yankin Arewa ta tsakiya damar samar da shugaban jami’iyyar APC na kasa.

Talla

Bayan murabus din Abdullahi Adamu wanda ya fito jihar Nasarawa, maimakon a mayar da kujerar a yankin, sai aka ba Ganduje wanda ya fito daga yankin Arewa maso Yammacin Nijeriya, wanda a cewarsa hakan ya saba wa kundin tsarin jami’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...