Atiku ya yabawa Fubara bisa kawo ƙarshen siyasar ubangida a jihar Rivers

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, a ranar Lahadi, ya ce sakamakon zaben kananan hukumomin jihar Ribas ya kawo karshen cin zarafi da siyasar ubangida a jihar.

Atiku ya ce wannan zai da damar yiwa al’umma aiki yadda ya dace kuma damar bin kundin tsarin mulki a jihar.

Talla

Ya yabawa gwamna Sim Fubara na jihar Ribas kan sakamakon zaben kananan hukumomin da aka kammala a jihar.

A 2027 za mu sallami Kwankwaso daga Siyasa – Doguwa

Atiku ya ce sakamakon zaben ya nuna cewa Fubara ya nuna jajircewarsa ga muradun jama’a da kuma kare martabar zaben kananan hukumomi.

Talla

Sanarwar da Atiku ya sanyawa hannu ta ce: “A yayin da aka kammala zaben kananan hukumomi a jihar, an kawo ƙarshen tsoratarwar da ake yiwa gwamnan, wanda hakan zai ya bayar da damar fara gudanar da kyakkyawan shugabanci a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related