Kwankwaso ya karɓi yan APC sama da 960 zuwa jam’iyyar NNPP a Kano

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Sama da mambobin jam’iyyar APC 960, karkashin jagorancin Alhaji Baba Sabiu, shugaban jam’iyyar a karamar hukumar Dala, sukw sauya sheka zuwa jam’iyyar NNPP.

Wannan sauya shekar na zuwa ne gabanin zaben kananan hukumomi da za a gudanar a ranar 26 ga watan Oktoba mai zuwa.

Wadanda suka sauya sheka da suka hada da tsaffin kansilolin mazabu 12 na karamar hukumar Dala, sun bayyana cewa suna bukatar ci gaba shi yasa suka koma jam’iyyar NNPP.

Talla

Alhaji Sabiu, a madadin sauran masu sauya shekar, ya bayyana cewa yana da kwarin gwiwar jam’iyyar NNPP za ta iya kawo sauye-sauye masu ma’ana, wadanda za su iya bata damar zashe duk wani da zabe da za’a yi nan gaba.

Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi wa sabbin ‘yan jam’iyyar barka da zuwa, inda ya tabbatar musu da cewa da su da wadanda suka dade a jam’iyyar duk daya suke.

Zaɓen ƙananan hukumomi: Gwamna Fubara ya Zargi Babban Sifeton Ƴansanda Nigeria da Yunkuri Tada Husuma a Rivers

Ya nanata kudurin jam’iyyar NNPP na bunkasa zamantakewa da tattalin arziki da siyasa a Najeriya, tare da mai da hankali sosai kan ajandar 2027.

Talla

“NNPP ta himmatu wajen inganta hadin kai da kuma ciyar da Nijeriya gaba,” in ji Kwankwaso, inda ya bukaci mazauna Kano da ‘yan Nijeriya baki daya da su marawa ‘yan takarar jam’iyyar baya a zabe mai zuwa.

Ya kuma yi kira ga yan Nigeria da su fito baki daya su marawa jam’iyyar NNPP baya, tare da jaddada manufar jam’iyyar na samar da dunkulalliyar Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...