Majalisar na neman sa kafar wando guda da shugaban ƙasa Tinubu

Date:

Daga  Isa Ahmad Getso

Majalisar wakilan Najeriya ta sa kafa ta rushe lambar girman da shugaban kasa Bola Tinubu ya bai wa shugaban ta Tajudeen Abbas na CFR.

Talla

‘Yan majalisar suka bayyana fusatarsu da ba shi lambar wanda suka bayyana ta a matsayin bata dace da girman kujerarsa ba, inda suka bukaci sauya masa da irin wadda aka bai wa shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ta GCON da kuma babban mai shari’a ta kasa.

Da dumi-dumi: Tinubu zai tafi hutu Burtaniya

Majalisar ta ce babu ban-banci tsakanin Akpabio da Abbas, saboda haka ya dace a bai wa shugaban su irin lambar da aka bai wa Akpabio ta GCON maimakon CFR.

Talla

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito shugaban ƙasa Bola Tinubu ya baiwa wasu mutane lambobin girmamawa na kasa, inda ya baiwa shugaban majalisar wakilai lambar yabo ta CFR, a jawabin da ya yiwa yan Nigeria a ranar cikar kasar Shekaru 64 da samun yancin kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...