Nigeria@64: Yan Nigeriya za su yi alfahari da ƙasarsu a karkashin gwamnatin Tinubu – Minista T Gwarzo

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane, Abdullahi Tijjani Gwarzo, ya taya shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu GCFR da daukacin ‘yan Najeriya murnar cikar kasar shekaru 64 da samun ‘yancin kai.

Ministan ya bayyana hakan ne a wani sako da ya aikewa ‘yan Najeriya na bikin zagayowar ranar samun ‘yancin kai ta bana, wadda mai taimaka masa kan harkokin yada labarai Adamu Abdullahi ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Talla

Ya ce yayin da Nigeria ke cika shekara 64 da samun ‘yancin kai, ‘yan Najeriya na da dalili yin murnar nasarorin da aka samu tsahon Shekaru 64.

“Duk da cewa kasancewar a matsayin kasa mun yi tafiya mai tsauri kuma mai sarkakiya, amma da jajircewar shugabanninmu, Najeriya ta samu gagarumin ci gaba a matsayinta na kasa mafi karfin tattalin arziki da dimokuradiyya a nahiyar Afirka”, in ji Ministan.

Yancin kai: Muhimman bangarori 6 na jawabin shugaban ƙasa Bola Tinubu

Ministan ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, yana bakin kokarinsa wajen gyara matsalolin kasar, yana mai cewa an bullo da tsare-tsare kuma an bullo da ayyuka da dama kuma ya himmatu don magance matsaloli da dama da kasar ke fuskanta.

Minista Gwarzo, ya bayyana cewa ma’aikatarsu ta gidaje da raya birane tana ci gaba da gudanar da shirin gina gidaje na “sabunta fata” da nufin tabbatar da cewa kowane mutum ya samu gida mai aminci, mai araha, mai daraja ba tare da la’akari da jinsi ko matsayi ba.

Talla

Don haka Ministan ya yabawa ‘yan Najeriya bisa yadda suke baiwa cigaban dimokaradiyya goyon bayan a ƙasar nan, ya mai cewa nan da yan shekaru masu zuwa ƙasar nan zata abar alfahari a karkashin gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...