Gwamnatin Jigawa za ta kafa cibiyoyi 27 na maida ababen-hawa su zama masu amfani da CNG

Date:

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa, ya bayyana shirin kafa cibiyoyin maida ababen-hawa zu zama masu amfani da iskar Gas (CNG) a fadin kananan hukumomi 27 na jihar.

Namadi ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Hamisu Gumel, ya fitar a yau Alhamis a Dutse.

Talla

Gwamnan wanda ya yi magana a wajen kaddamar da wani gidan mai na Safa and Fresh International Limited a jiya Laraba a Dutse, ya ce za a kafa cibiyoyin na CNG ne tare da hadin gwiwar kamfanin.

Gwamnatin Kano ta ciyo bashin makudan kudade don inganta ruwan sha

Namadi ya ce kafa cibiyoyin CNG zai rage kashe kudade da ake wajen sayen man fetur da kashi 60 cikin 100, inda ya kuma kara da cewa hakan zai taimaka matuka ga mazauna jihar.

Talla

Ya ce shirin zuba jarin ya yi dai-dai da ajandar gwamnatinsa guda 12, da nufin samar da ayyukan yi da bunkasar tattalin arziki.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...