Gwamnatin Jigawa za ta kafa cibiyoyi 27 na maida ababen-hawa su zama masu amfani da CNG

Date:

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa, ya bayyana shirin kafa cibiyoyin maida ababen-hawa zu zama masu amfani da iskar Gas (CNG) a fadin kananan hukumomi 27 na jihar.

Namadi ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Hamisu Gumel, ya fitar a yau Alhamis a Dutse.

Talla

Gwamnan wanda ya yi magana a wajen kaddamar da wani gidan mai na Safa and Fresh International Limited a jiya Laraba a Dutse, ya ce za a kafa cibiyoyin na CNG ne tare da hadin gwiwar kamfanin.

Gwamnatin Kano ta ciyo bashin makudan kudade don inganta ruwan sha

Namadi ya ce kafa cibiyoyin CNG zai rage kashe kudade da ake wajen sayen man fetur da kashi 60 cikin 100, inda ya kuma kara da cewa hakan zai taimaka matuka ga mazauna jihar.

Talla

Ya ce shirin zuba jarin ya yi dai-dai da ajandar gwamnatinsa guda 12, da nufin samar da ayyukan yi da bunkasar tattalin arziki.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...

Neman Ilimin addini dana boko da sana’a ba kishiyoyin juna ba ne – Dr. Aminu Sagagi ga matasan Zango

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malamin addinin musulunci a kano...