Dalilin da ya sa ‘yan kasuwar mai a Nigeria suka gwammace sayan man a NNPCL maimakon matatar Dangote – PENGASSAN

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar gas ta Najeriya, PENGASSAN, ta yi karin haske kan dalilan da suka sanya manya dillalan man fetur a Nigeria ke kasa sayen man fetur kai tsaye daga matatar Dangote.

Daily Trust ta ruwaito cewa shugaban kungiyar Festas Osifo a wani taron manema labarai a Legas a ranar Talata, ya ce lamarin ya samo asali ne daga sabanin farashin da aka samu tsakanin kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL) da kuma farashin da yake sayarwa ga ‘yan kasuwa masu zaman kansu.

Talla

Osifo ya bayyana cewa kamfanin na NNPC na iya siyan man akan N950, amma ya sayar wa ‘yan kasuwa masu zaman kansu akan kusan N700, wanda hakan zai haifar da gagarumin gibi da NNPC ke cikewa.

Ya ce idan manyan ‘yan kasuwa za su sayi man kai tsaye daga matatar Dangote to zasu saye shi ne akan farashi irin daya da yadda NNPCPL take siya, ka ga dole za su bukaci a sayar da shi a kan farashi mai yawa, mai yuwuwa sama da N1,000.

Yan sa-kai sun hallaka Ƙasurgumin dan ta’adda a jihar Zamfara

‘Yan kasuwa masu zaman kansu sun gwammace su sayi man daga NNPCPL don cin gajiyar rahusar da kamfanin yake yi musu, in ji shi.

Talla

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito an sha yin dambarwa tsakanin kamfanin man fetur na Nigeria NNPC da Matatar Ɗangote kan yadda farashin man zai Kasance, daga karshe dai kamfanin na NNPP ya fara siyan man fetur na matatar Ɗangote a ranar 15 ga wannan watan na Satumba akan farashin naira 898.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...