Tinubu Na Shirin Sauke Wasu Ministocinsa

Date:

 

 

Shugaba Bola Tinubu, ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) yau a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, yayin da ake ci gaba da raɗe-raɗin cewar zai sauke wasu ministocinsa.

Rahotanni da dama sun nuna cewa Tinubu na shirin yin wasu sauye-sauye nan ba da jimawa ba, bayan ya yi barazanar sallamar wasu ministocinsa da ba su taka rawar gani ba.

Sarki Sanusi II ya yi raddi masu sukarsa game da sanya kafet mai sunan “Muhammadu” a dakin karantunsa

Duk da haka, shugaban ƙasar bai tabbatar da takamaiman lokaci ko yadda sauyin zai kasance ba.

A taron majalisar, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya jinjina wa Tinubu kan rawar da ya taka wajen tabbatar da sahihin zaɓe a Jihar Edo.

Ya kuma taya jam’iyyar APC, murna kan nasarar da suka samu a zaɓen Sanata da aka gudanar kwanan nan a jihar.

Talla

Akume, ya kuma sanar da majalisar game da rasuwar tsohuwar Ministar Harkokin Mata, Salome Jankada, wadda ta rasu a ranar 27 ga watan Agusta.

Majalisar ta yi ta’aziyya tare da girmamawa ga tsohuwar ministar.

Manyan jami’an gwamnati irin su Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkar Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, da wasu ministoci sun halarci taron.

Sai dai hankali ya karkata kan yiwuwar Tinubu na sauya ministocinsa a nan gaba kaɗan.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...