Nasarar APC a zaɓen Edo ta nuna yan Nigeria sun gamsu da salon mulkina – Tinubu

Date:

Shugaban kasa Tinubu ya taya murna ga dan takarar jam’iyyar APC, a zaben Gwamnan jihar Edo, Sanata Monday Okpebholo bisa nasarar lashe zaben da ya yi.

A juya Lahadi ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, ta sanar da Sanata Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

A sanarwar da mai baiwa shugaban kasa shawara kan fannin yada labarai da dabarun mulki , Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya yabawa shugabannin APC na kasa da na jihar Edo da Gwamnonin jam’iyyar bisa aiki tukuru wajen nasarar ta a zaɓen.

Kwalejin Sa’adatu Rimi: Tsohon kwamishinan ilimi zamanin Kwankwaso ya kalubalanci gwamnatin Kano

Shugaban ya ce, nasarar ta nuna goyan bayan da al’umma ke bai wa manufofin gyaran tattalin arziki, da ma salon mulkin da APC.

Shugaban ya kuma yi kira ga wadanda su ka samu rashin nasara da su yi amfani da hanyoyin shari’a wajen mika kokensu.

Talla

Shugaban ya kuma godewa INEC da jami’an tsaro bisa tabbatar da an yi zaben cikin nasara.

“Ina yabawa hukumar zabe ta INEC da hukumomin tsaro bisa aiki ba dare ba rana wajen gudanar da zaben cikin lumana”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...