Iftila’i: Yara hudu sun mutu a cikin firinji

Date:

 

Wasu yara huΙ—u sun mutu lokacin da suke wasa a cikin wani tsohon firinji a yankin Zambezi da ke arewa maso gabashin Ζ™asar Namibia, inda tuni Ζ³ansanda su ka fara gudanar da bincike kan lamarin.

BBC ta rawaito cewa yaran masu shekara uku zuwa shida, an gano su ne a cikin firijin da aka daina amfani da shi a yankin mai cike da cunkoso a garin Katima Mulilo a jiya Litinin da yamma.

Rundunar β€˜yan sandan ta yi imanin cewa yaran sun maΖ™ale ne a lokacin da suke wasa, inda suka faΙ—a ciki, amma ana ci gaba da bincike.

Tinubu ya fi Ζ™arfin satar dukiyar Najeriya β€” Minista

Biyu daga cikin yaran sun mutu nan take a cikin firijin yayin da sauran biyu kuma suka mutu a asibiti lokacin da suke karΙ“ar magani, kamar yadda kafafen yaΙ—a labarai a yankin suka ruwaito.

Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Maryam Abacha Ta Jajantawa Al’ummar Maiduguri, ta nemi yan Nijeriya su kai musu dauki

β€œLokacin da na shigo, na ga jami’an lafiya na kula da Ι—iyata da wata yarinya. Sun garzaya da su asibiti, yayin da sauran biyun kuma aka saka su cikin motocin Ι—aukar gawawwaki,” in ji Aranges Shoro, mahaifin yaran, akmar yadda ya shaida wa wata jaridar Ζ™asar ta Namibia.

An sanar da mutuwar sauran yaran biyu bayan garzaya da su asibitin Katima Mulilo da ke kusa, kamar yadda kafar yada labarai ta NBC ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related