Ambaliyar Ruwa: Sarki Aminu Bayero ya jajantawa al’ummar Maiduguri

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana ibtila’in ambaliyar ruwan da aka samu a Maidugurin jihar Borno da cewa wani babban abu ne da ya girgiza al’umar Kasar nan baki daya.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana hakan ne a sakonsa na jajantawa al’umar jihar Borno da Kasa baki daya bisa ambaliyar ruwan data faru a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran sarkin Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Iftila’i: Yara hudu sun mutu a cikin firinji

Yace ba kasafai aka fiya samun irin wannan mummunan ambaliyar ba, amma idan hakan ya faru to babu abunda ya kamata ga al’uma sai yin addu’ar Allah Kada ya sake maimatawa.

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu ya kuma bada lafiya ga wadanda suka jikkata tareda mayar da mafificin alheri ga wadanda suka rasa dukiyoyinsu.

Daganan mai Martaba Sarkin ya sake Mika jajensa ga Shugaban Kasa chief Ahmad Bola Tinubu da Mataimakinsa Alhaji Kashim Shetima da Gwamnan jihar Borno Professor Baba Gana Umara Zulum da Shehun Borno Alhaji Mustapha El Garbai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...