Ambaliyar Ruwa: Sarki Aminu Bayero ya jajantawa al’ummar Maiduguri

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana ibtila’in ambaliyar ruwan da aka samu a Maidugurin jihar Borno da cewa wani babban abu ne da ya girgiza al’umar Kasar nan baki daya.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana hakan ne a sakonsa na jajantawa al’umar jihar Borno da Kasa baki daya bisa ambaliyar ruwan data faru a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran sarkin Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Iftila’i: Yara hudu sun mutu a cikin firinji

Yace ba kasafai aka fiya samun irin wannan mummunan ambaliyar ba, amma idan hakan ya faru to babu abunda ya kamata ga al’uma sai yin addu’ar Allah Kada ya sake maimatawa.

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu ya kuma bada lafiya ga wadanda suka jikkata tareda mayar da mafificin alheri ga wadanda suka rasa dukiyoyinsu.

Daganan mai Martaba Sarkin ya sake Mika jajensa ga Shugaban Kasa chief Ahmad Bola Tinubu da Mataimakinsa Alhaji Kashim Shetima da Gwamnan jihar Borno Professor Baba Gana Umara Zulum da Shehun Borno Alhaji Mustapha El Garbai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...