NNPC ya fitar da farashin da yan Nigeria za su rika sayan man fetur din Ɗangote

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL) ya sanar da cewa farashin man fetur, na iya tashi sama da N1,000 kowace lita a gidajen Mai.

A cikin wata sanarwa a ranar Litinin, Kamfanin NNPC Ltd ya fitar da kiyasin farashin man fetur (wanda aka samo daga matatar Dangote akan farashin watan Satumba na 2024) a fadin kasar.

Da dumi-dumi: NNPC ya bayyana farashin da ya sayi Man fetur din Ɗangote

Sanarwar ta bayyana farashin man kamar haka Legas, N950 kowace lita; Sokoto, N992 kowace lita; Oyo, N960 kowace lita; Kano, N999 kowace lita; Kaduna, N999 kowace lita; FCT, N992 kowace lita; Rivers, N980 kowace lita; da Borno, N1019 kowace lita.

Kamfanin ya ce bisa tanadin dokar masana’antar man fetur (PIA), ba gwamnati ce ta kayyade farashin man fetur din ba, sai dai ana tattaunawa kai tsaye tsakanin bangarorin da abun ya shafa.

YANZU-YANZU: Obasanjo Ya Isa Minna, Domin Gana wa da IBB, Abdulsalami, Gusau

“ NNPC ta tabbatar da cewa ta sayo kashin farko na man a matatar Dangote da dalar Amurka, Sannan ta ce zai fara siyan man da Naira ne daga ranar 1 ga Oktoba, 2024.

Hukumar NNPC ta bayar da tabbacin cewa idan aka sami ragen kudin man ba zata yi kasa a gwiwa ba wajen ragewa kuɗin ga yan kasa don su sami sauki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...