Da dumi-dumi: NNPC ya bayyana farashin da ya sayi Man fetur din Ɗangote

Date:

Kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL) ya bayyana cewa ya sayi man fetur a kan Naira 898 kan kowace lita daga matatar Dangote.

Kamfanin mai ya kai kwashe kimanin manyan motoci 300 zuwa matatar mai da ke Legas, ranar Asabar, kuma an fara lodin a ranar Lahadi.

YANZU-YANZU: Obasanjo Ya Isa Minna, Domin Gana wa da IBB, Abdulsalami, Gusau

Da yake zantawa da daily trust kan farashin man fetur din, Kakakin Hukumar NNPC, Olufemi Soneye, ya ce, “Mun yi nasarar fara lodin man fetur a matatar Dangote a yau. Batun cewa mun sayi man fetur din akan Naira 760 a kowace lita ba gaskiya ba ne. Wannan lodin na farko, daga matatar Ɗangote sun sayi kowacce lita akan Naira 898 ne.”

Ya shaida wa daily trust cewa, ya zuwa lokacin hada wannan rahoton an yi lodin manyan motoci sama da 70.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...