Dole yan Nigeria su dawo daga rakiyar siyasar ubangida wajen zaɓen shugabanni — Shekarau

Date:

 

 

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce dole ne a dawo daga rakiyar siyasar ubangida domin zaɓen shugabanni nagari.

Sanata Shekarau ya kuma yi Allah wadai da yadda wasu ‘yan siyasa ke dakile kwararar romon dimokuradiyya ga ayyukan gwamnati a Nijeriya ta hanyar yin watsi da ƙa’idojin gudanar da ayyukan da suka rataya a wuyansu.

Shekarau ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da ƙasida mai taken, ƙalubalen gudanar da harkokin siyasa daga jami’an gwamnati’ a wani taro na kwanaki 4 da aka shirya wa mambobin hukumar yi wa ma’aikata hidima ta ƙasa (NASC) da manyan jami’an gudanarwa na majalisar tarayya da aka fara a Abuja ranar Juma’a.

Yanzu-yanzu: An rage kudin shiga zaɓen kananan hukumomi na Kano

Shekarau ya ce maganganun da shugabannin siyasa ke yi a bainar jama’a don burge magoya bayansu ya saɓa wa ƙa’idojin aikin gwamnati.

Sojojin Nigeria sun Kashe Ƙasurgumin Dan ta’adda da ya addabi Arewacin Nigeria

Ya ƙara da cewa, naɗe-naɗen siyasa da ba su da muhimmanci kuma waɗanda ba su zama dole ba, na ƙara yawan kashe kuɗaɗe da hakan yana haifar da ruɗani a ayyukan jama’a.

A cewarsa, batun shugabanci shi ne babban jigon nasara na kowace ƙungiya ko al’umma.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...