Ambaliyar Maiduguri: A hukumance NEMA ta fitar da adadin mutanen da suka rasu

Date:

 

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya, NEMA ta ce kimanin mutum 37 ne suka mutu sakamakon mummunar ambaliya ruwa da ta auka wa birnin Maiduguri.

Yayin zantawarta da BBC shugabar hukumar Hajiya Zubaida Umar ta ce akwai fargabar ƙaruwar waɗanda iftila’i ya shafa, yayin da ma’aikatan hukumar ke cigaba da aikin ceto waɗanda suka maƙale.

Hajiya Zubaida ta kuma ce fiye da mutum 400,000 suka rasa muhallansu sakamakon bala’in.

Asibitin Best Choice Ya Kaddamar Da Sabuwar Na’urar Jarirai Ta (Jaundice) Irinta Ta Farko A Arewacin Najeriya

Shugabar hukumar NEMAn ta kuma bayyana ambaliyar a matsayin mai tayar da hankali.

“Abin akwai tashin hankali, don ruwa ya cinye garin Maiduguri ba kaɗan ba, ga mutane nan kana gani an koro su daga gidajensu”, in ji ta.

Ta ce ambaliyar ta cinye kusan kashi 40 cikin 100 na birnin Maiduguri.

Da dumi-dumi: Rarara Ya Dauki Nauyin Aikin Wani Titi a Jihar Kano

Hajiya Zubaida ta ce har kawo yanzu akwai mutanen da ba a iya ceto su ba bayan da suka maƙale cikin ɓaraguzan gine-gine.

Ta ƙara da cewa jami’an hukumar na ci gaba da aikin ceto mutanen da ambaliyar ta rutsa da su.

”Yanzu haka da nake magana jami’an hukumarmu a cikin unguwanni domin ci gaba da zaƙulo mutanen da har yanzu ke maƙale cikin gidajen da ruwa ya cinye”, in ji shugabar hukumar ta NEMA

Tuni da gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya ce fiye da mutum miliyan guda ne ambaliyar ta shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...