Ambaliyar da ta auku a 2024 ita ce mafi muni a shekaru 30 da suka gabata a Maiduguri, fadar Jihar Borno.
Wannan ambaliya ta samo asali ne daga ruwan sama kamar da bakin kwarya ta da aka tafka na tsawon kwanaki a Maiduguri da akasarin kananan hukumomin Jihar Borno.
Maiduguri da yankin Jere na daga cikin wuraren da lamarin ya fi kamari, inda a ranar Litinin Gwamnatin Jihar Borno ta rufe makarantun firamare da sakandare domin kare dalibai daga salwanta.
Daga bisani, a ranar da dare, lamarin ya sanadiyyar fashewar Madatsar Ruwa ta Alau mai nisan kilomita 10 daga garin Maiduguri.
Yadda ambaliyar ruwa ta mamaye gidaje a Maiduguri
ِA cikin dare ruwan ya fara mamaye unguwanni, inda kafin wayewar gari yawancin unugwannin garin suna cikin ruwa, a wani yanayi da shekaru 30 ke nan rabon da ga irinsa a garin.
Da talatainin dare ne ambaliyar ta mamaye Fadar Shehun Borno da tituna da gidaje da gadojin da sauran wurare, lamarin da ya tilasta wa jama’a sauya matsuguni.
Ya ce ruwan ambaliyar ya yi ƙarfin gaske inda ya mamaye Fadar Shehun Borno, Kofa Biyu, Gadar Fori wadda ta haɗa Fori da Galtimari zuwa Tashan Bama.
A cewarsa, unguwannin da lamarin ya fi ƙamari sun haɗa da Fori, Galtimari, Gwange, da Bulabulin.
Ambaliyar ta mamaye Fadar Shehun Borno, hadi da raba dubban mazauna unguwannin Post Office, Gwange, Moromoro, Gadar Customs, Gidan Zoo, Bulabullin, Maidoki Roundabout, Jami’ar Maiduguri, Cocin Saint Patrick da sauaransu da muhallansu.
Da talatainin dare ne ambaliyar ta mamaye Fadar Shehun Borno da tituna da gidaje da gadojin da sauran wurare, lamarin da ya tilasta wa jama’a sauya matsuguni.
Ya ce ruwan ambaliyar ya yi ƙarfin gaske inda ya mamaye Fadar Shehun Borno, Kofa Biyu, Gadar Fori wadda ta haɗa Fori da Galtimari zuwa Tashan Bama.
A cewarsa, unguwannin da lamarin ya fi ƙamari sun haɗa da Fori, Galtimari, Gwange, da Bulabulin.
“Kowa ya kaurace wa yankin post office, kasuwar Monday Market zuwa zoo da gidan man Hissan saboda ambaliya ta riga ta shanye su, mota ba ya iya bi,” in ji Refeal.
“Da mislain 12:30 aka sanar da mu cewa mu kwashe ’yan kananan kayan da za mu iya, amma kafin mu ciro takardun shaidar karatumu, har ruwan ya kawo mana mara,’ in ji wani mazaunin Galtimari.
Iftila’i: Yadda muggan dabbobi suka shiga cikin al’umma a maiduguri sakamakon ambaliyar ruwa
Bilyaminu Yusuf, ya ce, “muna cikin mawuyacin hali a Lagos Street, ambaliya ta sa mu hijira zuwa makarantar Firamare ta Galtimari mun bar kayanmu a gida.”
Wakilinmu ya gano yadda ruwan ya shanye Gadar Lagos Street, daya daga cikin manyan gadojin da ke garin Maiduguri.
Hakazalika gidan radiyo da talabijin na jihar (BRTV) Post Office, Shehu Laminu way, da unguwar Custom su ma ambaliyar ta shafe su.
Wani ma’aikacin BRTV ya wallafa a Soshiyal Midiya cewa, “ruwa ya shanye ofishinmu da Post Office.”