Sojojin 196 sun ajiye aiki a Najeriya

Date:

 

Aƙalla sojojin Najeriya 195 sun mika takardun ajiye aiki domin ƙashin kansu ga Rundunar Sojin Najeriya.

Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya ba ta bayyana dalilin ajiye aikin sojojin ba, amma wasu majiyoyi sun danganta lamarin da rashin ƙwarin gwiwa a tsakanin sojoji, sakamon matsin rayuwa a ƙasar.

Mai magana da yawun rundunar, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu, ya ce Babban Hafsan Sojin rundunar ya amince da aniyar sojojin ta barin aiki domin ƙashin kansu.

Zaɓen 2027: Kwankwaso Ya Bugi Kirji

Nwachukwu ya ce sojojin sun bi ka’ida kuma dokar aikin soji ta tanadi hakan, don haka, za su fara hutun barin aiki daga ranar 1 zuwa 24 ga watan Nuwamba, 2024.

Sanarwar da Birgediya-Janar O.H. Musa ya sanya wa hannu ta ce murabus ɗin sojojin zai fara aiki ne daga ranar 30 ga watan na Nuwamba.

Nwachukwu ya bayyana cewa rundunar ta yanke tattara jerin sojojin 195 da za su bar aiki don ƙashin kansu domin sallamar su a lokaci guda ne saboda ta yi musu kyakkyawan tsari kamar yadda ta saba a tsawon shekaru.

Ya ce hakan ya ba da damar bin dukkan ka’idoji da yin shirye-shiryen biyan su kuɗaɗensu na sallama da kuma fara karɓar fanshonsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...