Yanzu-yanzu: Hukumar Zaɓe ta sauya lokacin yin zaɓen kananan hukumomin Kano

Date:

Daga Mukhtar Yahya Shehu

 

Hukumar zabe Mai zaman kanta ta jihar Kano ta sauya lokacin gudanar da zaben kananan hukumomin jihar zuwa watan oktoba.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban hukumar faefesa Sani Lawal Malunfashi ne ya sanar da haka yayin Taron masu ruwa da tsaki a Shelkwatar hukumar.

Cigaban karamar hukumar Rano ne ya sa na fito takarar ba don kashin kaina ba – Dr. Isma’il Yusuf Musa

Ya ce sauya lokacin ya biyo bayan bin umarnin kotun koli na tabbatar da ‘yancin gashin Kai ga kananan hukumomin kasar nan daga watan oktoba Mai zuwa.

Faefesa Sani Lawal Malunfashi ya ce hukumar ta Sanya ranar 26 ga watan oktoba na wannan shekara sabanin yadda a baya ta Sanya ranar 30 ga watan Nuwamba Mai zuwa.

Ya ce sauya lokacin gudanar da zaben ya shafi dukkanin lokutan da hukumar ta fitar da suka shafi zaben a baya.

Talla
Talla

Shugaban hukumar zaben ta jiha ya ce za a fara yakin neman zabe daga ranar 1 gq watan satunba sai Kuma zabukan fitar da gwani daga jam’iyyu daga ranar 3 zuwa 14 ga watan satunba yayin da Kuma za a fara sayar takardun neman tsayawa takara ranar 15 ga watan satunba zuwa 26 ga watan satunba.

Farfesa Sani Lawal Malunfashi ya ce za a gudanar da zaben kananan hukumomin jihar Kano da kansilolin su ranar Asabar 26 ga watan oktoba na wannan shekara yayin da hukumar za ta sanar da sanar da sakamakon zaben ranar 27 ga wata oktoba na wannan shekara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...