Bayan Tsige Aminu Black Gwale, Ibrahim Soja Kantin Kwari ya zama Shugaban kungiyar APC Media Forum Gawuna Garo

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Jam’iyyar APC reshen jihar kano ta nada Ibrahim Soja Kantin Kwari a matsayin sabon shugaban kungiyar APC Media Forum Gawuna Garo.

Ida za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito kungiyar ta shiga cikin ruɗani ne tun lokacin da tsohon shugaban kungiyar Aminu Black Gwale ya umarci ‘ya’yan Kungiyar da su dakata daga kare jam’iyyar APC da jagororinta na jihar kano.

Wadancan kalamai sune suka yi Sanadiyar Aminu Black Gwale ya rasa kurarsa, kuma bayan sauke shi an nada Hon. Ibrahim Soja Kantin Kwari a matsayin sabon shugaban kungiyar APC Media Forum Gawuna Garo.

Badakalar magunguna: Abubunwan da muka gano bayan kama Dan Kwankwaso da wasu mutum 4 – Muhuyi Magaji

Sakataren jam’iyyar APC na jihar kano Hon. Ibrahim Zakari Sarina ne ya jagoranci rantsar da Ibrahim Soja a matsayin sabon shugaban kungiyar APC Media Forum Gawuna Garo.

Sabon shugaban dai zai rike Shugabanci kungiyar ne a matsayin Shugaban riko kafin daga bisani a gudanar da zabe.

Da yake jawabi bayan karbar rantsuwar kama aiki, Ibrahim Soja ya godewa shugabannin jam’iyyar APC na jihar kano bisa goyon bayan da suka bashi har ya zama Shugaban kungiyar.

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam’iyyar APCn Kano

” Ina ba ku tabbacin zan tsaya tsayin daka don ganin ya’yan wannan kungiya sun kare kima da martabar jam’iyyar ta APC da kuma jagororin mu masu daraja”. Inji Soja Kantin Kwari

Ya ce zai yi duk mai yiwuwa don ganin ya’yan wannan kungiya sun sami hakkokinsu tare da samar musu da walwala, don samin nasarar da aka sanya a gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...