Idan zanga-zanga ta ƙazance to fa za mu ɗau mataki — Sojoji

Date:

Babban Hafsan Tsaro (CDS), Christopher Musa, ya ce sojoji za su shigo ciki idan zanga-zangar ‘#EndbadGovernance’ da ke ci gaba da gudana a fadin kasar ta ci gaba da rikide wa zuwa tashin hankali.

Musa dai na mayar da martani ne kan barna da sace-sace da aka yi a zanga-zangar da aka yi a sassa da dama na kasar a ranar Alhamis.

Talla
Talla

Ko a ranar ma sai da aka farfasa cibiyar sadarwa ta musamman ta NCC a Kano, inda aka sace kayaiyaki na biliyoyin Naira.

Da yake zantawa da manema labarai a jiya Juma’a, Musa ya bukaci masu zanga-zangar da su gane cewa barna ba ta da amfani kuma zai jefa al’ummar kasar cikin rudani.

Atiku ya jinjinawa masu zanga-zanga, ya bukaci Tinubu ya saurari koken jama’a

Yayin da yake yabawa rundunar ƴansandan Najeriya bisa kokarin da take yi na tabbatar da zaman lafiya, ya kara da cewa za a tilastawa sojoji shiga lamarin idan har aka ci gaba da samun tashin hankali.

Ya ce: “Ya kamata mu gane cewa wadannan barna da kudaden mu aka samar da su kuma da kudaden mu za a gyara su idan kuka bata.

“Don haka maimakon yin haka, ya kamata mu hada kai don tabbatar da cewa babu wani abu. ya lalace,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...