Dan Iliyasu Satame da al’ummar Obajana za su shiryawa Ɗangote saukar al’qur’ani 10

Date:

Daga Sadiya Abba Dala

 

Kamfanin Dan Iliyasu Satame Global Enterprise da hadin gwiwar wasu yan uwa daga garin Obajana sun shirya taron saukar karatun al’qur’ani mai girma har guda goma da zummar Allah Subhanahu wata’ala ya kara ciyar da kamfanin Ɗangote gaba.

Alhaji Aliko Ɗangote dai shi ne mamallakin rukunonin kamfanin Ɗangote, kuma wanda ya fi kowa arziki a Nahiyar Africa.

Zanga-zanga: Kwamitin zaman lafiya ya yi Allah-wadai da lalata kaddarori a Kano

Kamfanin na Dan Iliyasu Satame Global Enterprise ya ce ya shirya taron saukar al’qur’anin ne da addu’o’in Allah ya kara yalwata arzikin Ɗangote saboda yadda yake tallafawa al’umma ba a Nigeria ka dai ba har da sauran kasashen Africa.

A sanarwar da Babban Nura ya aikowa kadaura24, za a gudanar da taron saukar ne a ranar lahadi 28 ga watan almuharram, 1446. Wcce ta zo daidai da 04 ga watan Ugusta 2024.

Za a gudanar da taron ne a zawiyar Alhaji Umaru Tanko Obajana da misalin karfe 10 na safe.

Sanarwa daga Baban Nura

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...